Na farko 1
Shekarunsa suna raguwa amma baya tuhumar kansa akan haka. Idan kudinsa ya ragu xai tuhuma bayan kudi yana dawowa amma shekaru basa dawowa.
Na biyu 2
Kullum yana cin arzikin Allah in halal yaci za'a tambaye shi in haram ne za'ayi masa azaba akai bai san karshen hisabin mai zai kasance ba.
Na uku 3
Kullun yana kusantar lahira yana nisantar duniya amma duk da haka baya damuwa da lahira kamar yadda ya damu da duniya Bai san makomarsa ba shin Aljanna ce ko wuta.
GASKIYA
Babu abunda zai amfane ka sai sallar ka/ki da kyawawar aikin ka/ki.
Duniya kwana uku(3) ce;
Jiya: Mun ganta ba zata dawo ba.
Yau: Muna cikinta ba zata dauwama ba zata wuce.
Gobe: Bamusan ina zamu kasance ba.
Ka kyautata wa kowa, ka zauna da kowa lfy, ka yawaita Afuwa da sadaka domin ni da kai dasu duk Matafiya ne.
Bissalam!!!
BARKANMU DA WARHAKA

No comments:
Post a Comment